The news is by your side.

Iran Ta Yi Barazanar Kai Hari kan Sojojin Amurka Bayan Hare-Hare kan Tankokin Mai a Tekun Oman

21

Rundunar kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta yi gargaɗin cewa duk wani sabon hari kan tankokin man Iran ko jiragen kasuwanci a Mashigin Hormuz zai haifar da “mummunan hari” kan cibiyoyin sojin Amurka da jiragenta a yankin.

Rahotanni sun ce barazanar ta zo ne ranar Asabar yayin da rikicin Tehran da Washington ke ƙara tsananta a yankin Tekun Fasha.

A cikin wata sanarwa da rundunar IRGC ta wallafa a shafinta na X, rundunar ruwan IRGC ta ce, “Gargaɗi! Duk wani hari kan tankokin man Iran da jiragen kasuwanci zai haifar da mummunan hari kan ɗaya daga cikin cibiyoyin Amurka a yankin da kuma jiragen abokan gaba.”

Jim kaɗan bayan haka, rundunar sararin samaniyar IRGC ta bayyana cewa makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa na Iran sun riga sun saita wuraren sojin Amurka da jiragen ruwa a yankin.

Sanarwar ta ce, “Makaman IRGC Aerospace Force da jiragen yaƙi marasa matuƙa sun riga sun saita wuraren Amurka da jiragen abokan gaba a yankin. Muna jiran umarnin harba su.”

Barazanar na zuwa ne bayan tashin hankali da hare-hare kan tankokin mai a Tekun Oman da kuma ƙarin fargabar faɗaɗar rikici a Mashigin Hormuz, wanda ke daga cikin muhimman hanyoyin safarar mai a duniya.

Leave A Reply

Your email address will not be published.