The news is by your side.

APC Ta Tantance Ƴan Takarar Majalisar Dokokin Rivers, Ta Kori 65 Masu Alaƙa Da Gwamna Fubara

39

Kwamitin tantance ƴan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) domin zaɓen majalisar dokokin Jihar Rivers ya amince da ƴan takara 33 tare da hana wasu 65 shiga zaɓen fidda gwani na jam’iyyar gabanin babban zaɓen 2027.

Kwamitin tantancewar, wanda Muraina Ajibola ya jagoranta, ya bayyana cewa mutane 98 ne suka sayi fom domin neman kujeru 32 na majalisar dokokin jihar Rivers.

Rahoton kwamitin, wanda Ajibola, sakataren kwamitin Ishaku Tanko Yamawo, Aisha Abdullahi Adamu da Danjuma Samuel suka sanya wa hannu, ya ce an kori ƴan takarar ne saboda rashin cika sharuɗɗan tantancewar.

A cewar rahoton, daga cikin dalilan da suka sa aka hana wasu shiga har da zargin bayar da cin hanci ko ƙoƙarin bayar da shi, gabatar da takardun shaida marasa sanya hannu, rashin gabatar da katin zaɓe da kuma rashin nuna katin ko takardar shaidar zama mamba a jam’iyya.

Kwamitin ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin waɗanda aka hana sun gabatar da bayanan haihuwa masu karo da juna, lambobin kasancewa ɗan jam’iyya marasa inganci, rashin isassun masu gabatar da takara da kuma rashin daidaito a sunayen da ke cikin takardunsu.

Rahoton ya ƙara da cewa wasu takardun da aka gabatar ba su ƙunshi muhimman bayanai na kan takardun shaidar NECO ba.

Kwamitin ya ce ya gudanar da aikin tantancewar cikin gaskiya, tsari da kuma bai wa kowa dama.

“An gayyaci dukkan ƴan takara su bayyana a gaban kwamitin tare da asalin takardunsu da sauran bayanan da suka gabatar wa jam’iyya tun da farko,” in ji rahoton.

“An bai wa kowane ɗan takara damar kare kansa tare da amsa tambayoyin da suka shafi ilimi, gogewar siyasa, zama mamba a jam’iyya, masu gabatar da takara, alaƙa da mazaɓa da sauran muhimman bayanai.”

Kwamitin ya ce ya kuma binciki shaidun halartar ayyukan jam’iyya da matsayin kasancewarsu mambobi.

Rahoton ya nuna cewa daga cikin waɗanda aka hana shiga akwai wasu da ake dangantawa da gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, da tsohon ɗan takarar gwamna na APC, Tonye Cole.

Daga cikin fitattun magoya bayan Fubara da ba su tsallake tantancewar ba akwai Chijioke Ihunwo, Victor Oko-Jumbo da Sokari Goodboy.

Rahoton ya kuma zargi Victor Oko-Jumbo da haddasa rikici a wajen tantancewar bayan ya nace wajen shiga tare da jami’an tsaro.

Kwamitin ya bayyana cewa dukkan ƴan takara 33 da aka amince da su ana kallonsu a matsayin masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike.

Jam’iyyar APC ta jihar Rivers ta buƙaci ƴan takara su duba sakamakon tantancewar a allon sanarwar jam’iyyar.

Sakataren yaɗa labaran APC a Jihar Rivers, Chibike Ikenga, ya ce za a karɓi ƙorafe-ƙorafen ɗaukaka ƙara kan tantancewar ta hannun sakatariyar jam’iyyar a ranar 12 ga watan Mayu.

A halin da ake ciki, ana ci gaba da tambayoyi kan matsayin tantancewar gwamna Siminalayi Fubara gabanin zaɓen 2027.

Da yake magana kan batun, sakataren jam’iyyar APC na ƙasa, Ajibola Basiru, ya ce kwamitin tantancewar ne zai fitar da rahotonsa bayan kammala aikin.

“Ina ganin duk wanda ya bayyana a gaban kwamitin tantancewa ya bi wani muhimmin ɓangare na tsarin,” in ji shi.

“Bayan kammala ganin duk waɗanda ya kamata ya gani, kwamitin zai zauna domin fitar da cikakken rahoto.”

Leave A Reply

Your email address will not be published.